KIRKIRA
Matashi a Kano ya kirkiri injin gyaran shikafa
by admin on | 2024-03-17 17:01:32 Last Updated by admin on2026-02-22 10:30:36
Wani matashi mai suna Abdullahi Danjuma dake karamar hukumar Dala a jihar Kano ya kirkiri injin gyaran shinkafa wanda ke cire tsakuwa tare da sissika baki daya.
Wannan matashi yace ya samar da wannnan inji ne saboda masu karamin karfi musamman mutanen kauye masu noman shinkafa, wannan inji zai saukaka musu wajen sarrafa shinkafa sannan al umma zasu sameta da sauki.
A cewar wannan matashin kasashe dayawa suna amfani da fasahohi na gida domin cigaban al ummar su tareda samun saukin rayuwa.